Gwamnan Katsina ya ba da umarnin dakatar da malami kan zargin neman ɗaliba

0
307

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umaru Radda ya bayar da umarnin dakatar da wani malamin makarantar sakandare bisa zargin sa da laifin neman ɗaliba da niyyar lalata.

Hakan na ƙunshe ne a wata takarda da gwamnan ya rubuta wa kwamishinar ilimi a matakin farko ta jihar, Hadiza Yar’adua.

Umarnin gwamnan na zuwa ne bayan samun rahoton cewar malamin, wanda shi ne shugaban makarantar da ke a ƙaramar hukumar Dandume, na neman ɗalibai mata.

Sanarwar wadda ta samu sa hannun daraktan yaɗa labaru na ofishin sakataren gwamnatin jihar, Abdullahi Faskari, ta kuma buƙaci da a yi bincike kan zargin da ake yi wa malamin tare da ɗaukan matakan da suka dace.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here